GABATARWA
Dukkan yabo ya tabbata ga Ubangiji, tsira da aminci su kara
tabbata ga fiyayyen halitta annabi Muhammad tare da iyalansa tsarkaka.
Wannan littafi yana dauke da tambayoyi guga casa’in (90)
tare da amsoshinsu game da halifa na uku, wato imam Husaini (a.s), tun daga
haihuwarsa har zuwa shahadarsa. An fito da wadannan tambayoyi ne sakamakon
musabakar da aka yi wa daliban makarantar Hauzatu Bakiril’ulum (a.s) da ke Dambare
ranar Tasu’a ta shekarar 2013 miladiyya a Husainiyyar da ke makarantar.
Mun
fito da tambayoyin ne muka mayar da su littafi domin sauran dalibai su amfana
da da su. Kuma wadannan tambayoyi da amsoshi an fassara su ne daga littafin KADATUNA.
Haka kuma hujjatul Islam walmuslimin Sheikh
Muhammad Nur shi ne ya duba wadannan tambayoyi.
MUJTABA
SHU’AIBU ADAMU
Hauzatu
Bakiril’ulum, Kano
10 –
10 - 2015
السلام على الحسين وعلى علي ابن الحسين وعلى أولاد الحسين
وعلى أصحاب الحسين
TAMBAYA
|
AMSA
|
|
1
|
A
wane wata aka haifi imam Husaini?
|
A
watan Sha’aban.
|
2
|
A
wace shekara aka haifi imam Husaini?
|
A
shekara ta hudu bayan hijira
|
3
|
Wace ce mahaifiyar imam Husaini (a.s)?
|
Nana
Fadimatu (a.s)
|
4
|
Shekarun
imam Husaini nawa lokacin da ya yi shahada?
|
Shekarunsa
57.
|
5
|
A
ina aka haifi imam Husaini (a.s)?
|
A
Madina
|
6
|
A
ina aka binne shi?
|
A
Karbala
|
7
|
Ya
ake kiran ranar da imam Husaini ya yi shahada?
|
Ashura
|
8
|
Ya
sunan matar imam Husaini wadda ta haifi imam Aliyu Zainul Abidina?
|
Shazana
‘yar Yazdajir.
|
9
|
Nawa
ga wata imam ya yi shahada?
|
10
ga watan Muharram.
|
10
|
Su wane ne shugabannin samarin aljanna?
|
Imam
Hasan da Husaini
|
11
|
Mece
ce alkunyar imam Husaini (a.s)?
|
Baban
Abdullahi
|
12
|
A
zamanin wane sarki imam Husaini ya yi shahada?
|
Yazidu
dan Mu’awiya.
|
13
|
Imamai nawa ne daga ‘ya’yan imam Husaini?
|
Imamai
9 ne.
|
14
|
Hajji
nawa imam Husaini ya je da kafarsa?
|
Hajji
25.
|
15
|
Wa
imam Husaini ya aika zuwa ga mutanen Kufa?
|
Muslim
dan Akil.
|
16
|
Wane ne ya jagoranci rundunar da ta fara tare su imam
Husaini?
|
Hurru
dan Yazid Arriyahi
|
17
|
Yaya
sunan wanda ya fara harbin
imam Husaini da sahabbansa?
|
Umar
dan Sa’ad
|
18
|
Me Umar dan Sa’ad ya fadi lokacin da ya harbi su Imam
Husaini?
|
Ku shede ni a wajen sarki cewa ni ne na fara harbin
Husaini.
|
19
|
Sahabban Imam Husaini su nawa ne a filin Karbala?
|
Su
36 ne.
|
20
|
Wane
ne ya sari imam Husaini a hannunsa na hagu har ya cire shi?
|
Zar’atu
dan Shuraik Tamimi.
|
21
|
Wane
ne ya sare kan
imam Husaini (a.s)?
|
Shimru
dan Ziljaushan.
|
22
|
Wane
ne na karshen shahada a sahabban imam Husaini?
|
Suwai
dan abi Muda’i.
|
23
|
Wane
jagora ne daga rundunar Yazidu ya tuba ya komo cikin rundunar imam Husaini?
|
Hurru
dan Yazid Riyahi.
|
24
|
Wane
ne ya saura (namiji) daga rundunar imam Husaini ba a kashe shi ba?
|
Imam
Aliyu Zainul Abidina.
|
25
|
Karashe
fadin Imam Husaini: Ba zan yi muku bai’a da hannuna ba . . .
|
Ina
kaskantacce
|
26
|
Wane
ne ya jagoranci tawayen masu tuba (التوابين)?
|
Sulaimanu
dan Surd.
|
27
|
Wane
ne ya dauki fansar kisan imam Husaini?
|
Mukhtar
Assakafi.
|
28
|
Wane
ne sarki a garin Kufa lokacin da aka kashe imam Husaini?
|
Ubaidullahi
dan Ziyad.
|
29
|
Ta
yaya aka kashe Muslim dan Akilu?
|
An
sare kansa aka jeho shi daga kan
hasumiyar fada.
|
30
|
Wace
rana Muslim dan Akil ya yi shahada?
|
Ranar
8 ga Zulhijja.
|
31
|
Wasiku
nawa mutanen Kufa suka aika wa imam Husaini suna nemansa da ya tawo wurinsu
su taimake shi?
|
Wasiku
dubu arba’in.
|
32
|
Me
ya sa imam Husaini ya fita daga Madina?
|
Don
kada a halarta ta da kashe shi.
|
33
|
Me
aka yi alkawarin za a ba wa Umar dan Sa’ad idan ya kashe imam Husaini?
|
Za
a nada shi sarki a garin Rayyi.
|
34
|
Karasa
wannan taken: ... كل أرض
كربلاء؟
|
كل يوم عاشوراء ...
|
45
|
Wane ne ya biyo su imam Husaini ya yi tarayya da su?
|
Habibu
dan Muzahir
|
36
|
Wane
ne ya rike tutar imam Husaini?
|
Abbas
dan Ali
|
37
|
Me
imam Husaini ya ce da Hurru lokacin da ya zo ya tuba?
|
Kai da ne in Allah ya yarda a Duniya da Lahira.
|
38
|
Wane
ne ya fara fafatawa daga rundunar imam Husaini?
|
Abdullahi
dan Umair.
|
39
|
Me
imam Husaini ya tuna ana tsaka da yaki?
|
Ya
tuna Salla a farkon lokacinta.
|
40
|
Wane ne ya kashe Habibu dan Muzahir?
|
Hussaini
dan Tanitu.
|
41
|
Karasa fadin Aliyul Akbar: Ni ne Aliyu dan Husaini …
|
Na rantse da ubangijin Ka’aba mu ne muka fi cancanta da
annabi, wallahi dan dan karuwa ba zai mulke mu ba.
|
42
|
Me
ya sa ake kiran Ubaidullahi dan Ziyad da dan dan karuwa? Ko dan Kire?
|
Saboda
shi Ziyad dan karuwa ne, sai abu Sufyan ya karbe shi ya danganta shi ga
kansa.
|
43
|
Wane
jariri ne daga ‘ya’yan imam Husaini aka harbe shi da kibiya yana hannu babansa?
|
Abdullahi
dan Husaini.
|
44
|
Fadi
‘yan uwan imam Husaini biyu da aka kashe su tare da imam din.
|
Abdullahi dan Ali da Ja’afar dan Ali.
|
45
|
Karasa
fadin imam Husaini (a.s) ga wadanda suke yakarsu: “Idan ba ku da addini …
|
…ku zama ‘ya’ya a rayuwarku ta duniya”.
|
46
|
Wane ne ya harbi imam da kibiya?
|
Sinan
dan Anas Nakha’i.
|
47
|
Wane ne ya binne imam Husaini da sahabbansa?
|
Mutanen bani Asad tare da Zainul Abdina.
|
48
|
Mutum
nawa aka kashe daga ‘yan uwan imam Husaini ta bangaren mahaifinsa?
|
Mutum
shida.
|
49
|
Wane
ne ya kashe Abbas dan imam Ali?
|
Zaidu
dan Dauda da Hakim dan Dufail.
|
50
|
A
wace shekara aka yi tawayen Tawwabin?
|
Shekara
ta 65 bayan hijira.
|
51
|
Su wane ne ‘yan Tawwabin?
|
Wadanda suka tozarta imam Husaini kuma suka yi nadama
da hakan.
|
52
|
Wane
ne ya kashe Umar dan Sa’ad?
|
Mukhtar
Assakafi?
|
53
|
Me
ake nufi da: (قل تعالو ندع
أبناءنا)
a Alkur’ani?
|
Su ne: Hasan da Husaini.
|
54
|
Karasa fadin imam Husaini (a.s): “Na fito ne don neman…
|
…gyara a cikin al’ummar kakana”.
|
55
|
Karasa fadin imam Husaini (a.s): “Ba na ganin mutuwa
face rabauta …
|
…rayuwa (kuwa) da azzalumai illa tabewa.
|
56
|
Wane
ne mafi kankata daga ‘ya’yan imam ya yi shahada tare da imam Husaini (a.s)?
|
Alkasim
dan Husaini.
|
57
|
Su wane ne Ashabul kisa’i?
|
Manzon
Allah da Fadima da Ali da Hasan da Husaini (a.s)?
|
58
|
Me
ya faru da damkin kasar Karbala
wadda manzon Allah ya ba wa Ummu Salama?
|
Ta
zama jini lokacin da aka kashe imam Husaini.
|
59
|
Shekara
nawa imam ya rayu tare da kakansa manzon Allah?
|
Kasa
da shekaru bakwai.
|
60
|
Karasa
fadin manzon Allah ga imam Husaini: “Ya Allah ina sonsa …
|
…ka
so shi, ka so wanda yake sonsa”.
|
61
|
Sau
nawa imam Husaini ya yi hajji a kasa?
|
Sau
25.
|
62
|
A
gidan wa Muslim dan Akil ya sauka a garin Kufa?
|
A
gidan Mukhtar Assakafi.
|
63
|
Wane
ne mutanen Kufa suka tarbe shi da sunan shi ne imam Husaini (a.s)?
|
Ubaidullahi
dan Ziyad.
|
64
|
Wane
ne wanda imam Husaini ya ce: “An karya bayana” lokacin da aka kashe shi?
|
Dan
uwansa Abbas dan imam Ali.
|
65
|
Karasa
fadin mawaki: Yanzu al’ummar da ta kashe Husaini za ta so …
|
…ceton
kakansa ranar hisabi?
|
66
|
Wurare
nawa ake cewa an binne kan
imam Husaini a wurin?
|
Wurare
tara ne.
|
67
|
Shekarun
Abbas nawa lokacin da ya yi shahada?
|
Shekaru
34.
|
68
|
‘Yan
uwan Muslim dan Akil nawa ne suka yi shahada tare da imam Husaini (as.)?
|
Su uku ne: Abdullahi da Ja’afar da Abdurrahman.
|
69
|
Wane
ne daga Banu Hashim ya fara yin shahada a Karbala?
|
Ali
Akbar dan imam Husaini.
|
70
|
Me
imam Rida ya yi umarni a rinka cewa idan an tuna bala’in Karbala?
|
“Ina ma mun kasance tare da ku, da mun rabauta da
babban rabo”.
|
71
|
Habibu dan Muzahir yana daga cikin sahabban annabi?
|
Yana
cikinsu.
|
72
|
Shugaban wace kabila ne Habubu dan Muzahir?
|
Kabilar
Asad.
|
73
|
Wane
ne mafi kankantar shekaru a sahabban imam Husaini?
|
Amru
dan Jinadata mutumin Madina.
|
74
|
Wane
ne daga cikin jikokin imam Husaini ya jagoranci tawaye ga Umayyawa?
|
Zaidu da Ali da Husaini.
|
75
|
Imamai nawa ne suke da suna Husaini?
|
Mutum
daya ne.
|
76
|
Wadanne abubuwa ne suka fi soyuwa ga Yazidu?
|
Shan
giya da farauta da kare.
|
77
|
Nawa
ne adadin rundunar Umar dan Sa’ad?
|
Fiye
da 4000
|
78
|
Me
imam Husaini ya nema daga mutanensa da daddare kafin a fara yaki?
|
Ya nemi su sulale cikin dare.
|
79
|
Ya
sunan matar da ta boye Muslim dan Akin a gidanta?
|
Sunanta
Dau’a.
|
80
|
Me
‘ya’yan Muslim suka fada lokacin da suka sami labarin kashe mahaifinsu?
|
Sun
ce: “Wallahi ba za mu huta ba har sai mun dauki fansa ko kuma mu ma mu dandani
abin da ya dandana.
|
81
|
Wa
imam Husaini ya aika ya debo musu ruwa?
|
Dan
uwansa Abbas dan imam Ali.
|
82
|
Fadi
mutum biyu daga sahabban imamu Husaini da suka yi shahada tare da shi.
|
Muslim
dan Ausaja da Zuhairu dan Kain.
|
83
|
Wane
ne daga sahabban imam Husaini ya ce: “Tsakaninmu da ‘Hurul’ini’ (matan
aljanna) kawai wadancan su auko mana”?
|
Barbar
dan Hudair Hamdani.
|
84
|
Wane
ne farkon wanda ya yi shahada daga sahabban imam Husaini (a.s)?
|
Muslim
dan Ausaja.
|
85
|
Wane
ne ya harbi imam Husaini da kibiya a bakinsa?
|
Hussaini
dan Tanimu.
|
86
|
Wace mace ce ta yi Khuduba a Kufa bayan Zainab?
|
Fadimatu
‘yar imam Husaini.
|
87
|
Shekaru
nawa imam Husaini ya rayu tare da mahaifinsa imam Ali (a.s)?
|
Fiye
da shekaru 30.
|
88
|
Wace
aya imam Husaini ya rinka karanta ta
yayin fitarsa daga garin Makka?
|
(رب
نجني من القوم الظالمين)
Allah ka tseratar da ni daga azzaluman al’umma.
|
89
|
A
wane gari aka binne imam Husaini (a.s)?
|
A
Karbala.
|
90
|
Wane
imami ne bayan imam Husaini (a.s)?
|
Imam
Aliyu Zainil Abidina.
|
Comments
Post a Comment