TSARABAR YARA DAGA AHLULBAIT (A.S)



TSARABAR YARA
DAGA
AHLULBAITI (A.S)


 

NA




MUJTABA SHU’AIBU ADAMU
mujtabakano@yahoo.com
2009


GABATARWA SHEIKH NUR
Da sunan Allah mai rahama mai jin kai. Tsira da amincin Allah         su tabbata ga manzon Allah da iyalan gidansa tsarkaka.
            Wannan littafin da ke hannunka, an yi bayanin abubuwa ne a saukake, wanda wadannan abubuwan suna da muhimmanci ga dalibi ya san su. To kasantuwar marubucin ya yi gogayya da koyarwa na tsawon lokaci, wanda hakan ya ba shi damar sanin halin da yara dalibai suke ciki na bukatuwa ga akidu da za a saukaka musu fahimtarsu, don haka wannan marubucin namu ya yi hobbasa domin taimakawa a wannan fage.
            Muna fata Allah ya kara masa basira, kuma Allah ya sa ya zama guzuri a gare shi gobe kiyama.
Sheikh Muhammad Nur.
Shugaban Mu’assasar Rasulul A’azam (S.A.W)
 


GABATARWAR MAWALLAFI
Dukkan yabo ya tabbata ga Ubangijin talikai. Tsira da amincin Allah su kara tabbata ga annabi Muhammadu tare da iyalansa tsarkaka.
            Wannan littafi ya kunshi bayanan abubuwa uku: Ginshikan Musulunci da rassanssa da kuma Tarihi. Wanda aka rubuta shi da sassaukan salo domin saukaka wa yara fahimtar Akidar Musulunci ingantacciya, wadda ta zo daga Ubangijinmu ta hanyar annabinsa Muhammad (S.A.W), kana ta biyo ta kan Ahlulbait wato iyalan gidansa tsarkaka, wadanda Allah ya tafi da dukkan datti daga gare su, ya tsarkake su tsarkakewa.
            A karshe ina mai godiya tare da jinjina ga malamaina, musamman Sheikh Muhd Nur Shugaban Mu’assasar Rasulul A'azam (S.A.W) da Sheikh Bashir Lawal da Sheikh Saleh Muhd Sani da dukkanin ma'aikatanta da ‘yan uwana dalibai da ‘yan majamu’a baki daya.
            Allah ya sa mu dace.
Mujtaba Shu'aibu Adamu
Hauzatu Bakirul Ulum Kano



KASHI NA FARKO
AKIDAR MUSULUNCI
Yana da kyau yaranmu su haddace wadannan jumloli masu zuwa:
1.    Allah ne Ubangijinmu.
2.    Muhammadu ne annabinmu.
3.    Musulunci ne addininmu.
4.    Ka'aba ce alkiblarmu.
5.    Alkur'ani ne littafinmu.
6.    Dukkan Musulmi 'yan uwanmu ne.
1 – ALLAH NE UBANGIJINMU:
Kamar yadda muka san cewa gine-ginen da muke ciki ko kuma muke gani, da motocin da muke shiga ko kuma muke gani masu kyawun gani, haka nan suturun da muke sakawa masu kyawun launi ba su ne suka yi kansu ba, mun san cewa akwai wani kwararre da ya kera su da wannan kyawun da muke iya gani. To ita ma sama da muke gani mai fadin gaske, tare da rana da wata da taurari. Ga kuma kasa mai fadi da muke zaune kuma muke yawo a kanta, lallai akwai wanda ya halicce su da wannan yanayin da muke ganinsu.
To haka nan muma mutane da muke raye, muke numfashi, muke gani da idanu biyu, muke da hannaye biyu da kafafuwa biyu, lallai akwai wanda ya halicce mu.
To wane ne ya halicce mu?
Wannan da ya halicci sammai da kassai da rana da wata da koramu da dabbobi, shi ne ya halicce mu, wato ALLAH, shi ne Ubangijinmu kuma shi ne mai iko a kan komai, shi ne kuma ya halicci kowane abu domin ya yi hidima ga mutum, lallai Ubangijinmu ya girmama mu!
Ya cancanci mu gode masa, kuma mu bauta masa bisa cancanta domin wannan ni'ima da ya yi mana.
2 – MUHAMMADU NE ANNABINMU:
Kamar yadda kowane yaro yake bukatar uwa da uba, ko bukatar dalibi ga malamai, haka nan mutum yake bukatuwa ga annabi wanda zai shiryar da shi hanyar alkhairi, ya kuma hana shi bin hanyar da zai halaka. Allah madaukakin sarki ya aiko annabwa da dama, sai ya sanya mu a cikin al'ummar Annabi Muhammadu (S.A.W).



Annabawa Iri Biyu Ne:
·               Akwai annabawan da Allah ya aiko su zuwa ga mutanen wani gari ko kauye. Kamar su:
Annabi Hudu da Annabi Salihu da Annabi Yunus da Annabi Shu'aibu da Annabi Zakariyya da makamantansu.
·              Akwai kuma Annabawan da Allah ya aiko su domin su shiryar da dukkan mutanen duniya. Kamar su:
Annabi Nuhu (A.S) da Annabi Ibrahim (A.S) da Annabi Musa (A.S) da Annabi Isa (A.S) da kuma Annabi Muhammadu (S.A.W) annabin karshe, wanda babu wani annabi a bayansa, kuma shi ne annabin da Allah ya aiko mana, mu mutanen karshe har zuwa tashin Alkiyama.
3 – MUSULUNCI NE ADDININMU:
Sunan addinin annabi Muhammadu MUSULUNCI, don haka mu musulmi ne masu biyayya ga Muhammad annabin Allah (S.A.W), domin bin sa bin Allah ne, saba masa kuma saba wa Allah ne, shi ne wakilin Allah a tare da mu. Haka kuma muna yin biyayya ga iyalan gidansa domin su ne wakilansa a tare da mu, wadanda ya yi mana wasici da su, a bisa fadinsa cewa: Na bar muku abubuwan da idan kuka yi riko da su a bayana ba za ku bata ba: Littafin Allah da iyalan gidana.
MECE CE KALMAR SHAHADA:
 (أشهد أن لاإله إلا الله, وأشهد أن محمدا رسول الله).
MA'ANA:
NA SHAIDA BABU ABIN BAUTAWA DA GASKIYA SAI ALLAH, KUMA ANNABI MUHAMMADU MANZONSA NE.
 Duk wanda ya furta wannan kalma yana mai imani da ita ya zama Musulmi, jininsa da dukiyarsa da mutuncinsa ya haramta a taba masa, sakamakonsa yana ga Allah. Kamar yadda ya zo a hadisi ingantacce daga manzon Allah (S.A.W).
4 – KA'ABA CE ALKIBLARMU:
Dukkanin Musulmi dakin Allah mai alfarma na Ka'aba suke fuskanta su yi salla, na kusa da na nesa da ita, salla ba ta inganta sai da fuskantar alkibla. Har yau a dakin ne Allah ya wajabta a yi aikin Hajji, ba ya halatta a yi aikin a wani wuri daban.
5 - ALKUR'ANI NE LITTAFINMU:
Hakika Allah madaukakin sarki ya saukar da litattafai ga wasu daga cikin annabawansa, domin ya zama shiriya ga al'ummarsu. Kamar: ATTAURA da INJILA. Littafin da aka saukar wa annabinmu Muhammadu (S.A.W) shi ne ALKUR'ANI mai girma, littafin shiriya ga wannan al'umma tun zamanin Annabi har ya zuwa tashin Alkiyama.

6 – DUKKAN MUSULMI 'YAN UWANMU NE:
   (أشهد أن لاإله إلا الله, وأشهد أن محمدا رسول الله).
Na shaida cewa: BABU ABIN BAUTAWA DA GASKIYA SAI ALLAH, KUMA ANNABI MUHAMMADU MANZONSA NE .  Wannan kalma ta hade dukkan Musulmi sun zama daya a wurin Allah, babu wanda ya fi wani a wurinsa, sai wanda ya fi jin tsoronsa.
Allah ya haramta zubar da jinin Musulmi ko cin mutumcinsa ko zaginsa. Ya kuma yi alkawarin sakayya ga duk wanda aka zalunta, a nan duniya ko a lahira.

GINSHIKAN MUSULUNCI
·         Ginshikan Musulunci guda nawa ne?
Ginshikan Musulunci guda biyar ne.
1.    Tauhidi.
2.    Adalcin Ubangiji.
3.    Annabta.
4.    Imama.
5.    Tashin Alkiyama.

·         Mene ne Tauhidi?
Shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah.
·         Mene ne Adalcin Ubangiji?
Shaidawa Allah maddukakin sarki mai adalci ne, ba ya zalunci.

·   Mece ce Annabta?
  Shaidawa Allah madaukakin sarki ya aiko annabawa, domin su shiryar da mutane zuwa ga alKhairi, na karshensu shi ne Annabi Muhammadu (S.A.W).
·         Mece ce Imama?
   Shaidawa manzon Allah ya yi wasici da imamai sha biyu a bayansa:
1.      Imamu Aliyyu.
2.      Imamu Hasan.
3.      Imamu Husaini.
4.      Imamu Aliyyu Zainul Abidina.
5.      Imamu Muhammadul Bakir.
6.      Imamu Ja’afar Assadik.
7.      Imamu Musa Al-Kazim.
8.      Imamu Aliyyu Rida.
9.      Imamu Muhammad Al-jawad.
10.  Imamu Aliyyu Al-Hadi.
11.  Imamu Hasan Al-Askari.
12.  Imamu Muhammad Al-Mahdi. (Wanda muke sauraro).



·         Mece ce tashin Al-Kiyama?
      Shaidawa Allah madaukakin sarki zai tashi mutane bayan mutuwarsu, domin ya yi musu hisabi a bisa abin da suka aikata a gidan duniya, na alkhairi ko na sharri.



KASHI NA BIYU
RASSAN ADDININ MUSULUNCI
·         Rassan addinin Musulunci guda nawa ne?
Rassan Addinin Musulunci guda goma ne.
1. Salla.                 2.  Azumi.       3.Zakka.      
4. Hajji.                 5. Humusi        6. Umarni da kyakkyawan aiki.  7. Hani da mummunan aiki.           
8. Jihadi saboda Allah.                  9. Tawalli.      
10. Tabarri.
·         Mece ce Salla?
Salla ibada ce da Allah ya wajabta wa musulmi sau biyar a rana. Su ne:
Ø Azahar                    Ø La’asar          
Ø Magariba                 Ø Isha’i                                 Ø Asuba
 Sallar Azahar raka’a nawa ce? 
Raka’a hudu ce.
v  Tahiya nawa?              Tahiya biyu.
v  Sallama nawa?            Sallama daya.
v  Karatunta a sarari ake yi ko a boye?    A boye.


v  Sallar La’asar raka’a nawa ce?           
Raka’a hudu ce.
v  Tahiya nawa?              Tahiya biyu.
v  Sallama nawa?            Sallama daya.
v  Karatunta a sarari ake yi ko a boye?    A boye.

v  Sallar Magariba raka’a nawa ce?        
Raka’a uku ce.
v  Tahiya nawa?              Tahiya biyu.
v  Sallama nawa?            Sallama daya.
v  Karatunta a sarari ake yi ko a boye? Biyun farko a sarari, dayan karshe a boye

v  Sallar Isha’i raka’a nawa ce?              
Raka’a hudu ce.
v  Tahiya nawa?              Tahiya biyu.
v  Sallama nawa?            Sallama daya.
v  Karatunta a sarari ake yi ko a boye? Biyun farko a sarari, biyun  karshe a boye.

v  Sallar Asuba raka’a nawa ce?
Raka’a biyu ce.
v  Tahiya nawa?              Tahiya daya.
v  Sallama nawa?            Sallama daya.
v  Karatunta a sarari ake yi ko a boye?    A sarari.
Salla ba ta yiwuwa sai da alwala, saboda fadin Allah madaukakin sarki:
﴿ياأيها الذين آمنوا إذا قمتم إلى الصلواة فاغسلوا وجوهكم وأيديكم إلى المرافق ومسحوا برؤوسكم وأرجلكم إلى الكعبين﴾.
YA KU WADANDA KUKA YI IMANI, IDAN KUN ZO YIN SALLA, KU WANKE FUSKOKINKU DA HANNAYENKU, KU SHAFI KAWUNANKU DA KAFAFUWANKU.
Wajiban alwala guda nawa ne?
            Wajiban alwala guda hudu ne.
  1. Wanke fuska.
  2. Wanke hannaye ya zuwa dantse.
  3. Shafar kai.
4.      Shafar kafafuwa[1].

NAJASA
Alwala ba ta yiwuwa sai an tsarkaka daga najasa. Akwai wasu abubuwan najasa da ya wajaba mu nisance su, kuma mu tsarkake jikkunanmu da tufafinmu da kayayyakinmu daga gare su.
Daga cikin su akwai: Fitsari da gayidi da kare da jini da makamantansu.
Idan najasa mai danshi ta taba jikin mutum ko tufafinsa, ya wajaba a gare shi ya wanke su da ruwa mai tsarki.



MISALIN YADDA AKE YIN SALLAR ASUBA
RAKA'A TA FARKO:
*      NIYYA: Ya kudurce a ransa cewa: Zai yi sallar Asubahi ta wajibi domin neman kusanci ga Allah.
*      KABBARAR HARAMA:  Bayan ya daidaita a tsaye ya ce: (الله أكبر) ALLAHU AKBAR  tare da daga hannayensa ya zuwa fuskarsa.
*      KARATUN FATIHA DA SURA:
بِسْمِ اللهِ الرَّحْمنِ الرَّحِيمِِ {1} الْحَمْدُ للّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ {2} الرَّحْمـنِ الرَّحِيمِ {3} مَالِكِ يَوْمِ الدِّينِ {4} إِيَّاكَ نَعْبُدُ وإِيَّاكَ نَسْتَعِينُ {5} اهدِنَا الصِّرَاطَ المُستَقِيمَ {6} صِرَاطَ الَّذِينَ أَنعَمتَ عَلَيهِمْ غَيرِ المَغضُوبِ عَلَيهِمْ وَلاَ الضَّالِّينَ {7}
Sannan ya karanta cikakkiyar sura, kamar:
بِسْمِ اللهِ الرَّحْمنِ الرَّحِيمِ{1}  إِنَّا أَعْطَيْنَاكَ الْكَوْثَرَ {2} فَصَلِّ لِرَبِّكَ وَانْحَرْ {3} إِنَّ شَانِئَكَ هُوَ الْأَبْتَرُ {4}
*       YIN RUKU'U:  Idan ya yi  ruku'un sai ya karanta wannan tasbihin sau daya:
(سُبْحَانَ رَبِّيَ العَظِيمِ وَبِحَمْدِهِ).
SUBHANA RABBIYAL AZIMI WABIHAMDIHI.
Ko (سُبْحَانَ اللهِ) SUBHANALLAHI. Sau uku.
*      DAGOWA DAGA RUKU'U: Ya ce:
(سَمِعَ اللهُ لِمَن حَمِدَه).
SAMI'ALLAHU LIMAN HAMIDAH.
*      SUJJADA TA FARKO: Bayan ya yi sujjada sai   ya karanta wannan tasbihin sau daya:
(سُبْحَانَ رَبِّيَ الأَعْلَى وَبِحَمْدِهِ).
SUBHANA RABBIYAL A'LA WABIHAMDIHI.
Ko (سُبْحَانَ اللهِ) SUBHANALLAHI. Sau uku.
*      DAGOWA DAGA SUJJADA TA FARKO: Ya zauna ya ce:    (اللهُ أكْبَر) ALLAHU AKBAR.
*      KOMAWA SUJJADA TA BIYU: Ya sake karanta wannan tasbihin sau daya:
(سُبْحَانَ رَبِّيَ الأَعْلَى وَبِحَمْدِهِ).
SUBHANA RABBIYAL A'LA WABIHAMDIHI.
*      DAGOWA DAGA SUJJADA TA BIYU: Ya zauna ya daidaita, kana ya ce: (الله أكبر) ALLAHU AKBAR. Wannan zaman shi ake kira da zaman 'Istiraha'.
Idan ya aikata haka, to ya yi raka'a guda cikakkiya, sai ya mike tsaye ya sake aikata kamar yadda ya yi a raka'a ta farko.
Mustahabbi ne ya karanta 'Alkunuti' bayan kare karatun sura ta biyu kafin ya yi ruku'u.
*      TAHIYA: Bayan ya dago kansa daga sujjada ta biyu a raka'a ta biyu, sai ya karanta tahiya kamar haka:
اَشْهَدُ أَنْ لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللهُ, وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ.
وَأَشْهَدُ أَنَّ مُحَمَّداً عَبْدُهُ وَرَسُولُهُ,
اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَآلِ مُحَمَّد.
ASHHADU ALLA'ILAHA ILLALLAHU, WAHDAHU LA SHARIKA LAH,
WA ASHHADU ANNA MUHAMMADAN ABDUHU WA RASULUHU,
ALLAHUMMA SALLI  ALA MUHAMMADIN  WA AALI MUHAMMAD.

Sannan ya yi sallama idan sallar mai raka'a biyu ce. Ya ce:
السَّلاَمُ عَلَيكَ أَيُّهَا النَّبِيُّ وَرَحْمَةُ اللهِ وَبَرَكَاتُهُ.
السَّلاَمُ عَلَيْنَا وَعَلَى عِبَادِ اللهِ الصَّالِحِينَ.
السَّلاَمُ عَلَيكُمْ وَرَحْمَةُ اللهِ وَبَرَكَاتُهُ.
ASSALAMU ALAIKA  AYYUHAN  NABIYU WA RAHMATULLAHI WA BARAKATUHU.
ASSALAMU ALAINA WA ALA IBADILLAHIS SALIHIN.
ASSALAMU ALAIKUM WA RAHMATULLAHI WA BARAKATUH.
Idan kuwa salla mai raka'a uku ce ko hudu, to ba zai karanta sallamar ba, sai a raka'a ta karshe1.
·         Mene ne Azumi?
Azumi ibada ne da Allah ya wajabta wa musulmi, kamewa daga barin abin ci da na sha a kwanakin watan Ramalana, daga fitowar alfijir zuwa faduwar rana ta shari'a.

·         Mece ce zakka?
Ita ce musulmi ya bayar da wani kaso kididdigagge, daga cikin dukiyarsa, ga talakawa da miskinai.

·         Mene ne Humusi?
Humusi shi ne, musulmi mukallafi ya bayar (1/5) daga cikin ribar da ya samu, a karshen kowace shekara.

·         Mene ne Hajji?
Hajji ibada ne da Allah ya wajabta wa musulmi mukallafi, sau daya a rayuwarsa, ga wanda ya sami iko.

·         Mene ne Umarni da kyakkyawan aiki?
Shi ne musulmi ya umarci mutane, ga aikata ayyukan alkhairi.


·         Mene ne Hani da mummunan aiki?
Shi ne  musulmi ya hana mutane, ga barin abin da Allah ya haramta.

·         Mene ne Jihadi?
Shi ne musulmi ya yaki zalunci da dukkan karfinsa.

·         Mene ne Tawalli?
Tawalli shi ne: Son masoya Allah.

·         Mene Tabarri?
Tabarri shi ne: Kin makiya Allah.




KASHI NA UKU
SIRAR SHUGABANMU ANNABI
MUHAMMADU (S.A.W)
Shi ne Muhammadu, dan Abdullahi, dan Abdul Mudallabi. Sunan mahaifiyarsa Aminatu 'yar Wahabi, sunan wanda ya raine shi Abu Dalibi, sunan wadda ta shayar da shi Halimatus Sa'adiyya, sunan danginsa Banu Hashimu.

MUTUWAR MAHAIFINSA
Mahaifinsa ya tafi fatauci ya zuwa Sham, a yayin dawowarsa, sai mutuwa ta riske shi a birnin Madina, sai aka binne shi a can, a sannan matarsa Aminatu tana da cikin Muhammadu wata biyu. A wannan ranar samarin Makka da manyan Larabawa, da yara da mataye da tsofaffi sun yi bakin cikin rabuwa da shi, tun ba matarsa ba Aminatu, da dan uwar haihuwarsa Abu Dalibi da mahaifinsa Abdul Mudallabi, sun hakura da abin da Allah ya kaddara musu, domin duk wanda Allah ya yi kiransa tilas ne ya tafi, rahamar Allah ta tabbata ga Abdulahi mahaifin manzon Allah.

HAIHUWARSA DA TARBIYYARSA
Yayin da shugabarmu Aminatu ta shiga cikin wata na tara da cikin manzon Allah, wani abu da yake samun mata kamar radadi da ciwon ciki bai same ta ba, ko wata kazanta ta wurin nakuda.
An haifi annabi Muhammadu a Makka abar girmamawa. Hakika kakansa Abdul Mudallabi ya yi matukar farin ciki da haihuwarsa, sai ya ambace shi da Muhammadu. A bisa al'adar Larabawa a kan bayar da lada a shayar da 'ya'yayensu a kauye, domin su tashi da fasahar Larabawa da rayuwar sahara mai tsanani.
A wannan lokacin Halimatu Sa'adiyya ta zo daga kauye ta nemi a ba ta Muhammadu domin ta shayar da shi. Ta kasance talaka, ba ta mallaki komai ba sai wasu 'yan tumaki kadan ramammu, sai aka ba ta Muhammadu ta tafi da shi.
Hakika albarkar Muhammadu ta lullube su lokacin da ta tafi da shi, sun ga alkhairi mai yawa da albarkatu, arziki ya lullube su, dabbobinsu suka yi nama da nono, suka yi farin ciki da Muhammadu abin shayarwa.
Muhammadu ya rayu a gidan Halimatus Sa'adiya tare da 'ya'yanta, sun so shi so mai tsanani, ya kasance kyakkyawa, mai hankali da ladabi. Yayin da ya kai shekara shida, sai ta zo da shi wurin kakansa da mahaifiyarsa Aminatu da shi. Suka gan shi ya zama saurayi, mai tsafta, abin so, suka yi farin ciki da shi. Sai aka ba wa Halimatus Sa'adiyya ladanta na shayar da Muhammadu tare da kyautatawa. Tsiran Allah da amincin Allah su kara tabbata a gare shi da iyalan gidansa.

MUTUWAR MAHAIFIYARSA AMINATU
Yayin da aka dawo da Muhammadu yana karami ya zuwa mahaifiyarsa, sai ta tafi da shi Yasriba (Madina), domin ziyartar 'yan uwanta kuma ta nuna musu Muhammadu. A tare da ita akwai mai yi mata hidima, wadda ake kira Ummu Aimana mutuniyar Habasha.
Lokacin da suka isa Yasriba, sai dangin mahaifiyarsa Aminatu suka tare su da farin ciki da annashuwa, suka zauna tsawon wata uku a birnin Madina.
A yayin dawowarsu zuwa Makka, sai mutuwa ta riski Amina bayan rashin lafiya, sai aka binne ta a can. Rahamar Allah da gafararsa su tabbata ga Aminatu. Sai Ummu Aimana ta tafi da shi ya zuwa kakansa Abdul Mudallabi, sai ya karbe shi ya ci gaba da tarbiyyarsa tare da ba shi kulawa. Ya kasance yana son Muhammadu so mai tsanani, ba ya rabuwa da shi.
Yayin da Muhammadu ya cika shekara takwas sai Abdul Mudallabi ya rasu, sai Abu Dalib ya ci gaba da rainonsa, ya kasance yana son Muhammadu sama da dukkan 'ya'yansa, ya raine shi tare da dukkan 'ya'yansa, har ya girma ya zama saurayi, sallallahu alaihi wa alihi wasallama.


AUREN ANNABI DA SAYYIDA KHADIJA
Yayin da annabi Muhammadu ya cika shekara ashirin da biyar, ya shahara da gaskiya da rikon amana, sai ya tafi fatauci ya zuwa kasar Sham da dukiyar nana Khadija tare da mai yi mata hidima, wanda ake kira Maisara.
Yayin da Muhammadu ya dawo daga Sham, sai Khadija ta ga albarka mai yawa tare da rikon amana a tare da shi, irin wanda ba ta taba gani a wurin wanin Muhammadu ba (S.A.W). Sai ta aika masa da ya aure ta, sai ya aure ta. Ta kasance  mace mai ladabi da biyayya ga annabi Muhammadu (S.A.W), ta sadaukar da dukiyarta wajen taimakon Addinin Musulunci.


TARIHIN IMAMU ALIYU (A.S)
Wane ne Imamu Aliyu?
Imamu Aliyu shi ne dan uwan Annnabi Muhammadu, wanda suke 'yan maza zur, kuma mijin shugabar matan duniya da Aljanna, nana Fadimatu 'yar annabi Muhammadu (S.A.W).
Sunan mahaifinsa Abu Dalibi, sunan wadda ta haife shi Fadimatu 'yar Asad.

HAIHUWARSA DA TARBIYYARSA
An haifi Imamu Aliyu ranar juma'a, uku (3) ga watan Rajab a cikin dakin Allah mai alfarma (a Ka'aba), kafin a aiko manzo da shekara goma sha biyu (12).
Lokacin da Fadimatu ta ji ciwon nakuda, sai ta shiga cikin Ka'aba mai alfarma, ta daga hannayenta ya zuwa sama, tana cewa: Ya Ubangiji na yi imani da kai da kuma dukkanin litattafan da ka saukar (ga manzanninka), na kuma gasgata kakana Annabi Ibrahim badadinka (A.S) shi ne ya gina (wannan) daki mai daraja. (Ya Allah na roke ka) domin wanda ya gina wannan daki da kuma abin da ke cikina ka saukaka mini wahalar haihuwa[2]. Ba ta kara ko sa'a guda ba ta haihu lafiya sumul kalau.
Yayin da imamu Aliyu ya cika shekaru hudu, sai annabi Muhammadu ya karbe shi, ya ci gaba da tarbiyyarsa na daga abin da Ubangiji ya sanar da shi, bai taba rabuwa da shi ba har ya koma ga mahaliccinsa.
Imam Aliyu ya yi imani da annabi Muhammadu bayan nana Khadija, wani abu na jahiliyya bai shafe shi ba.

GWARZONTAKAR IMAMU ALIYU
Imam Aliyu ya kasance wazirin annabi Muhammadu tun yana karami, ya bayar da dukkan karfinsa wajen taimakon manzon Allah, ya kasance yana biye da shi a duk inda yake, yana tare masa cutarwar yaran kuraishawa gwargwadon iko.
Bayan shekaru sha uku (13) da aiko Anabi Muhammadu, kafiran kuraishawa suka kulla makircin kashe Annabi, sai Allah ya umarce shi da yin hijira daga Makka zuwa Madina. Imam Ali ya bayar da rayuwarsa fansa ga Muhammadu (S.A.W), inda ya kwanta a shinfidar manzon Allah har annabi ya kubuta daga sharrin mushirikai.

JIHADINSA A MADINA
Imam Aliyu ya halarci dukkanin yake-yaken da aka yi da kafirai a zamanin manzon Allah, banda yakin Tabuka a bisa umarnin manzon Allah (S.A.W). Haka kuma ya bayar da gudummawa mai yawa a dukkanin yakokin.
Daga cikin yakokin da ya halarta, akwai: Yakin Tabuka da Uhdu, da Yakin Khandaku da Khaibara da bude Makka. Allah ya kara yarda a gare shi.


IMAMU ALIYU BAYAN WAFATIN
MANZON ALLAH
Hakika halifancin Muhammadu (S.A.W) hakkin Imamu Aliyu ne, saboda fadin manzon Allah: "Wanda na kasance shugabansa, Aliyu ma shugabansa ne". Sai dai yanayi bai ba shi damar karbar ragamar shugabancin a hannunsa ba, sai ya yi tarayya da sauran Musulmi wajen neman hadin kai don karfafa Musulunci.
Ya karbi shugabanci bayan kashe Usmanu dan Affana, ya yi mulki na shekara biyar (5), ya yi shahada a hannun Abdurrahmanu dan Muljamu (la'anar Allah ta tabbata a gare shi) a masallaci, aka binne shi a garin Najaf.


 MANAZARTA
* Assaiyid Hashim Musawi: Attarbiyyatul
       Islamiyya (na daya).
* Al’Islam Risalatuna Na Jam’iyyatu
      Ta’alimuddin Al’islami.
* Nafahatun Minassira Na Mu’assasar Albalagh.
* Kabasatun Minassira Na Munazzamatul
      Alamiyya Lilhauzat Walmadarisil Islamiyya


WARARE DA ZA A SAMI WANNAN
LITTAFIN
            1 – Hauzatu Bakirul Ulum (A.S) da ke Dambare Kano, a wurin: Abdullahi Muhammad Musa 07035858839.
            2 – Rasulul A’azam bookshop Tal’udu kusa da Dagedage supuer market Kano, a wajen: Nasiru Yusuf  08066667564.
            3 – Rahama bookshop kwanar taya titin kofar Dawanau daidai kwanar kutare Kano, a wurin: Malam Garbati 08066075031.


[1]  Lallai ne xalibai su sani cewa: Alwala ba ta yiwuwa sai da Niyya, hakanan dukkanin sauran ibadu. Sai an qudurce cewa za a yi alwalar ne domin neman yardar Allah ta'ala. Haka kuma alwala tana da sunnoni kamar:
·         Wanke hannaye zuwa 'ku'u' (wuyan hannu), sau xaya ko kuma sau uku.
·         Kuskurar baki, sau xaya ko sau uku.
·         Shaqa ruwa, sau xaya ko kuma sau uku.
1 Sai ya tashi ya kawo raka'a xaya sannan ya yi ruku'u (ko kuma ya karanta wannan tasbihin (سبحان الله والحمد لله ولااله إلا الله والله أكبر) sau xaya,  ko kuma ya karanta (سبحان الله) sau uku, kana ya yi ruku'u ya aikata kamar yadda ya yi a raka'o'in da suka gabata.
[2] Kashuf Gummati na Arbali. Babin ambaton Imamu Aliyu. Da kuma   Nafahatun Minas sira, na Mu'assatul Balahg  

Comments